Kungiyar Raya Auren Sunnah Ta Kasa

Kungiyar Raya Auren Sunnah Ta Kasa Kungiya ce da aka assasa ta don wayar da kai, haɗa aure, sada zumunta, wa'azantarwa, nishaɗantarwa da daidaita zaman takewar aure!

25/11/2023

Mu Girmama Malamai Ko da Muna da Saɓani da Su.

A wannan zamani da yawa daga ɗaliban ilmin, an samu ilmin ne kawai amma an rasa tarbiyyar ilmin, da mun ga malam wane ya saɓawa malam wane a wata fuska ta ilmi ko usulubi da yake bi wajen isar da sako ta saɓa ma hankali, sai mu kuma mu fito tare da munanan lafazin da suke tare da cin mutunci gare shi da sunan raddi ko bada kariya ma wanin mu.

Lallai ne yana da kyau, mu mutunta mutane da s**a ɗara mana a shekaru, musamman ma Maluma k**ar yadda hadisi yake cewa:

An ƙarɓo daga Ubaidah bin Samit yana cewa, Manzon Allah mai tsira da aminci ya ce: "Duk wanda baya mutunta manyan mu, baya tausaya ma ƙananan mu, kuma bai san haƙƙin malaman mu ba, to, wannan ba shi a cikin al'umma ta".

Imam Ahmad ne ya rawaito wannan hadisin daga Ubaidah bin Samit a cikin Musnadul-Ansar hadisi mai lamba 21693.

Shehun Malami Ɗawus bin Kaisan yana cewa: "Yana daga cikin Sunna a darajanta mutane huɗu, Malami, da tsoho mai furfura, da Sarki, da Mahaifi"
Albagwi ya kawo shi cikin Sharhus-Sunnah.

In fa ance mahaifi ba fa sai naka mahaifin ba, mahaifi suna ne gama gari na duk wanda ya haihu ba sai wanda ya haife ka ba, don cin mutuncin mai iyali cin mutuncin iyalansa ne.
Don haka, wajibcin Musulmi ne ya darajan ta Malami, ya mutunta shi, ya yi ladabi wajen ambaton sunan sa tare da yi masa addu'ar samun rahama da gafara daga Allah, ko malamin yana raye ne ko bayan ya mutu, kuma ba sai wanda kake so ba kawai, musamman in ya kasance fitacce ne wajen taimako gaskiya da yaɗa Sunna da tozarta ƙarya da tarwatsa ta.

Shehun Malami Abu Zur'ah Ar-Razi yana cewa: "Ina tare da Imam Ahmad bin Hambaliy sai aka ambaci sunan Ibrahim bin Ɗuhman, ɗaya daga cikin malamai na Allah, a lokacin shi Imam Ahmad ba shi da lafiya yana kwance amma nan take sai ya tashi ya zauna, ya ce, bai k**ata a ambaci mutanen kirki mu kuma muna kwance ba".
Tahzib Al Tahzib (1/148).

Allahu Akbar! Ka ji fa yadda magabata suke girmama malamai a gabannin idanun su da bayan su.

Allah Ka sa mu dace, Ka yafe mana kura-kuran mu.

Abu Abdir-Rahman Al-Fullaty!
11/Jumada ula/ 1445 Hijira.
25/11/2023 Miladiyya.

Ki Rike Min Mutuncin Ki,  Kin ji🧏Mutunci tafi zinariya da azurfaJiya bayan sallar Maghriba ina zaune kusa da mai POS a b...
19/09/2023

Ki Rike Min Mutuncin Ki, Kin ji🧏

Mutunci tafi zinariya da azurfa

Jiya bayan sallar Maghriba ina zaune kusa da mai POS a bakin Masallacin unguwar mu, sai ga wata yarinya ta zo karɓar kuɗin da ta sanya mahaifiyyar ta ta tura mata. Yarinyar irin sabbin tashin nan ne (kwaila) kan ta na f**a k**ar saurayin zakara, ba tare da gaisuwa ko sallama ba daga nesa ta fara aika kira ga mai POS kafin ta iso mu. Da ta iso sai mai POS yace mata mahaifiyyar ki ta tura miki 5k, sai ta ce haba 5k? Sai mai POS yace, ga kuɗin nan sai ki kira mahaifiyyar ku yi magana.

Mai POS ya mika mata wayar sa ta kira uwar nata. Ga hirar su k**ar haka da yake ta sanya shi a loud-speaker:

Yarinya: Assalamu Alaikum Mummy, ina wuni?

Mama: Wa'alaykumussalam, lafiya kalau yarinya ta, kin ga sakon ko?

Yarinya: Eh Mummy na gani, na gode Allah Ya daɗa buɗi

Mama: Amma me k**e yi haka da kuɗi, kwanan nan na tura miki da wani 5k, bana son ki riƙa sabo da kuɗi sosai fa.

Yarinya: Ina son in saya ma ƙanne na takalmi ne, don takalman su sun mutu.

Mama: Kina son kashe kuɗi dai na san ba lallai haka bane, ke dai ki kula, kuma duk abin da kika rasa ki yi min magana, kar ki je ga samari, ki kula da wannan.

Yarinya: In Allah yarda mama na gode sosai Allah Ya ƙara arziki.

Mama: A'a ni ce da godiya, tun da kin tsare min mutuncin ki, kuma ko nawa nake da shi zan baki, ni dai ki ji tsoron Allah, ki tsare min mutuncinki, kin ji?🧏

Yarinya: Ehem mama na gode, zan kula In Shaa Allah.

A haka tayi ta mata nasiha da gargaɗi har s**a yi ban kwana. Bayan ta gama wayar sai yarinyar na ga tamkar maganganun uwar ba shi ne ma a gaban ta ba, bisa ga alamar wani kalma da ta furta.

Ni kuwa sai na kira ta, don nasiha da soyayya da uwar take ga ƴar ta lokacin da suke wayar ba karamin daɗi na ji ba, sai na ce da yarinyar kin ga wannan nasiha da mahaifiyar take miji? Wallahi so take ki tsare mutuncin ki kan ki, kuma in kin tsare mutuncin kan ki, kin tsare na gidan ku ne da dukkan dangi, har ƴaƴan ki da jikokin ki, lallai ne wannan shi ne nasiha mafi tsada da uwa zata yi ma ƴar ta, kuma shi ne gatan da ba zaki iya samun shi bayan ta ba. Don haka ki amfani da maganar ta ki ji tsoron Allah, kuma ki ku ji munanan ƙawa.

Sai mai POS ya ce, kin ga wannan zamani in da kan ki ke rawan nan, in ba ki natsu ba da akwai matsala sai ya yi dariya, ita ma tayi dariya, amma sai tace zan kokari Malam na gode, amma duk natsuwar yarinya a wannan zamani hmmm...........

Ban ji sauran abin da ta ce ba, don na bar ta da mai POS, wanda shi ma da ta faɗi hakan kawai sai ta ruga a guje, yana cewa ta zo, amma ta arce bata tsaya ba.

Tabbas aiki na gaban iyaye a wannan zamanin. Allah Ya shiryar da mu, Ya shirya mana ƴaƴan mu, ƙannen mu da dukkan al-umma da muke rayuwa cikin ta.

02/11/2021

FARIN CIKIN ZUCIYA!
---------------------.
Mu'az bn Abdullah daga babansa, daga
baffansa cewa: Manzon Allah (Mai tsira da amincin Allah) ya fito
cikinsu da alamun ruwan wanka a jikinsa, yana tahe fuskarsa cike da farin ciki, mun yi tunanin ko ya jewa iyalinsa ne, sai muka ce da shi:
Ya Manzon Allah!
Mun ga ka fito cikin farin ciki, Sai yace:
"Haka ne kuma ina mai godiya ga Allah" sai aka ambaci wadata sai Manzon Allah yace : "Babu laifin wadata ga mai tsoron Allah. Amma lafiya ga mai tsoron Allah tafi wadata alkhairi, kuma farin cikin zuciya na daga cikin Ni'imah".
(Adabul Mufrad Hadith na 301).
Allah Ka sanya mu kasance cikin farin cikin zuciya da na zahiri a nan gidan duniya da kuma Lahira.

06/09/2021

Ita soyayya tamkar iska mai kaɗawa take, baka iya ganin ta, amma kana jin rasawar ta cikin jikin ka ko ta ina!
💘

05/08/2021

IDAN KA BI KA SHIRYU // 002

Kaɗan daga halayensa da koyarwarsa.

Kamar yadda muka shaida a rubutun mu da ya gabata cewa ta hanyar sanin Annabi (SAW) ne kawai za mu iya kaunarsa fiye da kawunan mu. Kuma sai mun sami wannan ilimi na saninsa da ƙaunarsa, sannan za mu iya gaya wa wasu gaskiya game da Annabin Musulunci mai tsira da amincin Allah.

Mutane da yawa a yau suna tattaunawa akan Annabi Muhammad ( SAW), suna son sanin:

Ko wane ne shi? Mene ne ya koyar? Me ya sa wasu ke matukar kaunarsa wasu kuma s**a tsane shi?
Shin ya cika da'awarsa? Shin mutum ne mai tsarkakakke? Shin ya Annabin Allah ne da gaske? Mene ne gaskiyar wannan mutumin?

A hanya mai saukin ta wanzuwar hankali za ka iya gamsar da mai wannan tunani ko tambayar waye Annabin Musulunci?

Mutane da yawa sun san Annabi Muhammad (SAW) da kan sa kuma sani na haqiqa, ga wasu kaɗan daga cikin abubuwan da aka zayyano game da shi:

• An haife shi ne daga wata ƙabila mai daraja ta Larabawa, wanda tsatsonsa ya haɗa da shugabannin Makka.

• Bai taɓa shiga cikin al'adar al'ummar kabilunsa na bautar wanin Allah, gumaka ko allolin ƙarya da mutun ya kirkira da hannunsa ba.

• Ya yi imani da cewa lallai Allah Shi ne Ubangiji kuma Mahalicci na gaskiya, don haka Shi kaɗai ya caccanta a bauta maSa, ba tare da wani “alloli” a tare da Shi ba.

• Ya yi riko da Umarnin Allah, k**ar yadda Annabawa s**a gabace shi s**a yi.

• Ya hana riba a lokacin ba da rancen kuɗi ne ko kayan noma da sauransu, k**ar yadda Yahudawa da Nasara s**a hana shekaru aru -aru kafin shi.

• Bai taba yin c**a ba kuma bai yarda ayi ba, sai dai ya yi nuni da haramcinsa.

• Bai taba shan giya ko abin sha mai ƙarfi ba; duk da cewa a lokacin tasowarsa abu ne na al'ada ga mutanen zamaninsa da wurin da yake rayuwa.

• Baya shiga gulma kuma ya kasance yana kau da kai daga jin ta, har daga bisa yayi hani gare ta da yaɗa jita-jita wanda suke haramun ne ga Musulmi.

• Ya koyar da Tsattsarkar labari da tsarki irin na Annabi Isah (AS) da haihuwarsa tare da mu'ujiza da mahaifiyar Maryam (AS) ta samu a lokacin cikinsa da ma hahuwarsa, kuma ya koyar da cewa Maryam tana cikin mafifitan dukkan halittun Allah.

• Ya yi umarni a bada zakka ga talaka da mai rauni kuma ya mai tsaro sannan garkuwar wuri kare haqqin zawarawa da mazajensu s**a mutu, marayu, matafiya da waninsu.

• Ya umarci mutane da su haɗa kai da danginsu kuma su girmama alakar dangi da alaƙa tsakanin 'yan uwa ta hanyar sadar da zumunta ga juna don karfafa danganta da soyayya tsakanin al'umma.

• Ya bukaci mabiyansa su shiga cikin alakar aure ta halal a tsakanin maza da mata ba mutu'a ba, kuma ya hana yin jima'i a wajen aure, don kauracewa fushin Allah.

• Ya dage kan bai wa mata haqqoqinsu da s**a dace na sadaki, gado da wasu dukiyoyinsu na halal da ma ƴancin magana a cikin sha'anin aurenta da sha'anin iyalanta da hana binne ta da ranta. Kai zuwan sa ne ma (SAW) ya baiwa dukkan ƴa mace ɗokacin daraja da kimar ta ta ƴa mace a tsakanin al'umma.

• Haƙurinsa da halin ƙasƙantar da kai abin koyi ne kuma duk waɗanda s**a san shi sun yarda da kyawawan halayensa da jin kansa da tsarkin zuciyarsa.

• Ya shahara a cikin dukkan kabilun Makka saboda kyawawan dabi'unsa.

• Ana kiran sa da Al-Ameen (Mai gaskiya da rikon amana) sabo da bai ta6a yin karya ba, bai ta6a cin amana ba kuma bai ta6a yin shaidar karya ba ko shaidar zur ba, illa ma yana yaƙar su ta hanyar hana aikata su.

• Ya hana kisa sai dai idan umarni ya zo daga Allah, kuma a sarari ya fitar da iyaka ga wanda za a iya kashewa. Ko a lokacin da ake yaƙi da waɗanda s**a ɗaga mak**ai ga Musulmi da Musulunci, ana yin yaƙi ne kawai bisa ƙa'idodi masu tsauri daga Allah.

• Bautar da mutane ta zama ruwan dare a wancan zamanin a cikin al -umma da dukkan nahiyoyi. Addinin Islama ya ƙarfafa mutane sosai don 'yantar da bayinsu kuma Allah Ya yi alƙawarin babban lada ga mutanen da s**a ƴan ta bayinsu don Allah. Annabi Muhammad (Mai tsira da amincin Allah) ya ba da misali ta hanyar 'yantar da bayi da kuma ƙarfafa duk mabiyansa su yi hakan.

• Baya rama sharri da sharri (SAW)!
Makiya sun yi wa Annabi mai tsira da aminci tsinuwa da kiran mugunta, amma ya amsa ta hanyar yi musu addu'ar shiriya. Babban misali na wannan shine tafiyarsa zuwa garin Ɗa'ifa. Shugabannin Ɗa'ifa sun ƙi sauraren shi ko kuma yi masa ladabi na al'ada da ake yi ma baƙi. Maimakon haka, sun sanya ƴan t**i su jefe shi, wadanda s**a yi ta jifansa da duwatsu har jikinsa ya yi jini. Mala'ika Jibrilu ya yi masa tayin fansa, wanda ya ce ya ba da umarni kawai, kuma Allah zai sanya duwatsun da ke kewaye su su faɗo su tarwatse musu a kai, ya hallaka su duka. Amma maimakon ya la'anta su ko ya nemi a halaka su, sai ya yi musu addu'ar shiriya don su sami damar bautawa Ubangijinsu, ba tare da abokin tarayya ba.

• Annabi Muhammad (Sallallahu Alayhi wa Sallam) ya koya wa mabiyansa imani da kyauta lafazi a dukkan lokacin da za su ambaci sauran Annabawar Allah k**ar su Adamu, Nuhu, Ibrahim, Yakubu, Musa, Dauda, ​​Sulaiman da Isah da sauransu, kuma ya nuna su a matsayin Annabawa na gaskiya, kuma Manzanni da sannan bayin Allah na haqiqa.

• Ya kuma koyar da cewa littattafan Attaura, Zabura da Injeela asalinsu wuri ɗaya ne da Qur'ani- kuma duk daga Allah ne, bai yarda mu aibanta guda daga cikinsu ba.

Wannan kaɗan ne daga halayya da ɗabi'u irin ta shi Sallallahu Alayhi wa Sallam.

Abou Abdir-Rahman Al-Fullaty!

26th / Dhul-Hijjah / 1442 Hijiriyya.

5th / August / 2021 Miladiyya.

IDAN KA BI SHI KA SHIRYU // 001TSOKACIKa yi tunanin wannan: A misali kuna wajen aiki, ko shaguna na saya da sayarwa, ko ...
05/08/2021

IDAN KA BI SHI KA SHIRYU // 001

TSOKACI
Ka yi tunanin wannan: A misali kuna wajen aiki, ko shaguna na saya da sayarwa, ko cikin motar haya zuwa wani unguwa ko gari. Kuna ji jin kunnuwar sai wasu baƙin mutane a wajen ku s**a zagi wanda ba ku sani ba. me ya k**ata ka yi a wannan lokaci? Babu komai?

Ko kuma: a misali sai ka ji ana zagin mahaifiyarka, ko mahaifinka, ko mijin ki, ko matarka ko ma dai ma wani da daga waɗanda kake so. me ka ke yi a wannan lokacin? Kana kare su? ko dai kawai kana haifar da hatsaniya akansu ko suna da gaskiya ko babu?

Me yasa muke tsaya musu? Saboda, muna son a girmama su? Ko sabo da daman babu wanda ke magana haka akan iyalin mu ko akan daidai na su ko kuskurensu? Ko dai kawai saboda mun san abin da aka faɗa akansu ba gaskiya ba ce; Ko kuma gaskiyar ce ta bamu damar da zamu kare su a kowanne hali? Ko kuma don gaskiyar ce muka ƙaunace su kuma muke kare su da barazanar tada hatsaniya a duk lokacin da aka ta6a su?

Ko ma dai mene ne, mu tafi kai tsaye da misalin mu kan cewa, a wannan lokacin muna jin wasu daga al'umma marasa daraja suna suƙa da aibanta Annabi mai tsira da amincin Allah, kuma hankularmu na tashi matukar ta shi, shin don Allah me ya k**ata mu yi a lokacin?

Kai tsaye dai a wannan ƙazamar duniya, babu ranar da zata shuɗe daga safiya zuwa maraice ko ma cikin dare wanda ba a zagin Manzon Allah (SAW) cikinta a kullum; a wurin aiki ne, ko a shagunan saya da sayarwa, da majisai na marasa daraja ko cikin abin hawa da muke tafiye - tafiye cikinsa. Ana aibanta shi a kafofin yaɗa labarai, ko taron 'yan siyasa, har ma a cikin wasu iyalai. Amma ta yaya muke mai da martani akan waɗannan munanan hare-hare da ƙarya gurbatattu akan wannan masoyin namu? Muna yin fushi ne kawai mu hatsala, ko kuma kawai shiru muke yi ba tare da mun yi ko tari ba? Ko dai kawai faɗa muke yi a hatsale ba tare da natsar da waɗannan baki masu aibanta shi ba? (SAW)

Abin baƙin ciki, muna yin duka abin da muka bayyana.
Muna yin hakan ne domin har yanzu Annabin bako ne a gare mu ko a zukatanmu. Muna da'awar muna ƙaunarsa amma halinmu yana ƙin kalmominmu.

Ba mu san ko wane ne shi ba har yanzu, ba mu san abin da ya tsaya akai ba sai dai hasashe, abin da ya koyar kuwa munyi nesa da ita don ƙaunarmu da duniya, abubuwan da ya aikata lokacin da abubuwa mak**ancin da aibatawa irin haka ya same shi kuwa kwata-kwata bamu kawo ta a zuciyar mu a lokuta masu yawa, to ta yaya ƙaunarmu gare shi za ta zame gaskiya?

Musulmi a farkon fari sun karbi musulunci ne sabo da sun yarda hankali da hali irin na Annabin Musulunci (SAW). Wasu sun girma tare da shi, sun san komai game da shi, kuma sabo da haka sun mika masa wuya, sun ƙaunace shi, sun ba shi komai, kuma sun misalta rayuwarsu a kansa, sun ba dukiyoyinsu, sun sadauƙar da iyalansu da iyayensu da jininsu akansa.

Lallai ne idan muna da'awar muna son Annabi Muhammad mai tsira da amincin Allah so na haƙiƙa, to ya k**ata mu ma mu san shi sani na haƙiƙa.
Wataƙila, da zarar mun san shi sosai, za mu ƙaunace shi fiye da uwaye da ubanninmu, mazajenmu da matanmu. Wataƙila za mu ƙaunace shi fiye da kanmu- kuma idan muka yi haka, to za mu gaskata da gaske muna ƙaunarsa.

Insha Allah zamu gabatar da rubuce-rubuce da muke fatan ya amfane mu kan soyayyar Annabin Rahma mai tsira da aminci Allah

Zamu yi kokarinmu don ganin mun hasko kaɗan daga halayensa, ɗabi'unsa, tausayinsa, haƙurinsa, juriyarsa, haƙurinsa, ƙaunarsa....... Insha Allahu hakan zai taimaka mana mu san shi, kuma mu ƙaunace shi Sallallahu Alayhi wa Sallam.

Da farkon fari dai a fara gabatar da ilimin sanin sa, sannan soyayyarsa ta biyo baya.

Allah Ya sa mu dace, Ya tsare mu daga afkawa cikin kura-kurai, Ya tsarkake niyyar mu.

Abou Abdir-Rahman Al-Fullaty!
23/Dhul-Hijjah/1442 Hijriyya.
2nd/August/2021 Miladiyya

Yaren Idanu A Fagen Soyayya👁👁  Mafi karfin sakon soyayya kan kwaranyo daga kogin idanu ne, su ne: "Gateways to the heart...
20/06/2021

Yaren Idanu A Fagen Soyayya👁👁

Mafi karfin sakon soyayya kan kwaranyo daga kogin idanu ne, su ne: "Gateways to the heart" a littafin: "How To Read A Person Like A Book", H. Calero ya ce: "Ta idanu ake tsinkar furannin son dake zuciya". Jalaluddeen Rumi cikin "Masnavi" ya ce: "Ana duban soyayya ne ta idanun zuciya".

A cikin kundin soyayya (طوق الحمامة) Ibn Hazm Al-Andalusy ya ce: "Soyayya na da wasu alamu da mai hikma ke saurin ganewa, na farko shi ne satar kallo da ke isar da boyayyen sakon zuci". Muftin soyayya "كريم الشاذلي" cikin bakandamen littafinsa (جرعات من الحب) ya ce: "Sanda murafen idanu s**a rungumi juna, busharar so na tafe".

Cikin allon rantsuwar soyayyar al'adun addinin Hindu a littafin: K**A SUTRA VATSYAYANA da ANANGA RANGA: Ratirahasya: secrets of love. Panchasakya: the five arrows. Smara Pradipa: the light of love. Ratimanjari: the garland of love. Rasmanjari: the sprout of love. Anunga Runga: the stage of love. Kamaledhiplava: boat in the ocean of love..... A hukunce-hukuncen so sun yi ittifaqi kan tasirin idanu, musamman ga matan da s**a kira: Padmini, Shankhini Hastini, Chitrini, Mrigi/Harini, Ashvini, Vadava da Karini.

Shi yasa in masoyi yai duban tsanakin sauraro zai ji idanun masoyiya na fadi: 'Habeby-Habeby' kuma tabbas shi ne mafi tsarkin zancen so. A littafin: "The Psychology of Persuasion" Robert B. Cialdini ya ce: "A sanda kauna ta yi kauna, ba bukatar kalamai dan isar da sako, lumsar idanu daga nahiya zuwa nahiya ya wadatar".

Fasihin mawakin Larabci ya ce cikin baitukan:

"وترمينني بالطرف أي أنت مذنب..وتقلينني لكن إياك لا أقلي"

Kina jifa na da gefen ido (magana), kai mai laifi ne.... Kina ki na, sai dai ni, ba zan taba kin ki ba.

Game da idanu, wani mawakin Larabci ya ce:

"إِنَّ العُيونَ الَّتي في طَرفِها حَوَرٌ. قَتَلنَنا ثُمَّ لَم يُحيِينَ قَتلانا. يَصرَعنَ ذا اللُبَّ حَتّى لا حِراكَ بِهِ. وَهُنَّ أَضعَفُ خَلقِ اللَهِ أَركانا". جرير

Ka ga duk idanun da s**a hada launi biyu: fari da baki, ga gira, s**an kashe mu, ba tare da ma mun san sun kashe mun ba. Su soooke mu, da tsinin ido, ba da tsinin mashi ba, su yi mana illa a zuciya. Su kan kayar da mutumin da yake mai dabara har ya kasa motsi, bayan kuma su s**a fi kowa rauni.

A daya daga poems dina wato: "My Dark-Eyed Damsel", na bayyana sindaren sakonnin kauna da idanu s**a kunsa k**ar yadda Rumi ya ce:

"The light which shines in the eye is really the light of the heart".

Ustaz Sadiq Madabo

(From the Archives)SHIN DOLE NE NA YI WA MIJINA HIDIMA?Ɗaukacin malaman Musulunci sun tafi akan cewa mustahabbi ne mace ...
20/06/2021

(From the Archives)

SHIN DOLE NE NA YI WA MIJINA HIDIMA?

Ɗaukacin malaman Musulunci sun tafi akan cewa mustahabbi ne mace ta kula da mijinta wajen yi masa hidima k**ar dafa abincinsa da sharar ɗakinsa da gyara masa makwancinsa da banɗakinsa da wankewa da goge masa tufafinsa da sauran abubuwan da a al’adance za a fassara su da sunan kulawa da miji.

Malamai suna ganin za ta yi hidimar koda kuwa ta kasance mace ce mai muƙami wacce a al’adance irinta, ba ta yin sauran ayyukan gidanta da kanta.

Sai dai akwai saɓani a tsakanin malamai ta fuskar tantance shin dole ne ta yi masa hidima ɗin ko kuwa ba dole ba ne?

Ɗaukacin malaman mazhabobin Shafi’iyyah da Hanbaliyyah da wasu cikin Malikiyyah sun tafi akan cewa ba dole ba ne mace ta yi wa mijinta hidima, amma ba laifi in ta yi abin da aka saba a al’adance cewa mace na yi wa mijinta.

Su kuwa malaman mazhabar Hanafiyyah sun doge ne akan cewa, aikin gidan miji dole ne akan matar aure.

Yayin da ɗaukacin malaman mazhabar Malikiyyah da Abu Thaurin da Ibn Abi Shaibah da wasunsu s**a tafi izuwa ga cewa, mace za ta yi wa mijinta hidima ne game da buƙatarsa ta cikin gida kawai. Amma duk abin da ya k**a sai an fita wajen gida, k**ar zuwa kasuwa da debo ruwa ko zuwa kai wanki da guga ko wani aiki mak**ancin haka ko kai sako da amsowa, to wannan ya fita daga abin da ake sa ran mace ta yi na kulawa da mijinta.

Malikiyyah sun ƙara da cewa, in mace ta kasance daga cikin
mata masu ɗaukaka waɗanda matsayinsu ya ɗara wa aikin gida, k**ar ‘ya’yan sarakuna da attajirai da duk wacce ta taso a gidansu cikin wadatar da take da masu yi mata aikace-aikace ko wacce ta sami wani matsayi a rayuwa k**ar babbar malama ko attajira ko mak**ancin haka. To, irin wannan miji bai da halin ya sa ta aikin gida sai in ta ga dama, ko kuma in ya kasance matalauci ne ba shi da halin samar mata da masu aiki.

Ibn Taimiyah yana daga cikin malaman da s**a zaɓi ra’ayin cewa dole ne matar aure ta yi wa mijinta hidima bisa abin da yake sananne a al’adar mutane. Sai ya ce: “Kuma ya wajaba a kan macce ta yi wa mijinta irin hidimar da aka san cewa irinta za ta iya yi ga irinsa. Kuma yanayin wannan hidima ya kan bambamta daga wuri zuwa wuri. [Alal misali] irin hidimar macen dake rayuwa a ƙauye ga mijinta ta bambamta da macen dake birni, irin hidimar da mace ƙaƙƙarfa za ta iya yi ta bambamta da wacce maras ƙarfi za ta iya yi”.

Haka shima Ibnul Ƙayyim ya tafi akai. A inda ya kawo hadisai da ke nuni izuwa ga haka, k**ar hadisin Fadima ‘yar Ma’aikin Allah (RA) wanda aka ba da labarin cewa ta kasance tana niƙa a gidan mijinta Aliyu (RA) har hannunta ya yi kanta da hadisin Asma’u matar Zubair (RA) wadda ta kasance tana yi wa mijinta hidima, har da kulawa da dokinsa; Ita ke yanko masa ciyawa ta ba shi ruwan sha sannan ta share ma dokin makwancinsa.

Sannan sai Ibnul Ƙayyim ya kwararo mazhabobin malamai da hujjojinsu, kafin a ƙarshe ya tiƙe izuwa ga cewa hidimar miji wajibi ce akan kowace matar aure, ba bambamci tsakanin ‘yar manya da ‘yar talaka, ko ‘yar sarki da ‘yar bawa, ko ‘yar masu kuɗi da ɗiyar matalauta ko malama da jahila da sauransu.

Uthaimin yana cewa: “dangane da aikin mace a gidan mijinta, wannan wani abu ne da ke komawa zuwa ga al’ada. Duk abin da a al’adance an saba mata suna yi wa mazajensu to shine abin da ya wajaba ta yi wa mijinta. Amma miji bai da ‘yancin ya tursasa wa matarsa yi wa mahaifansa hidima ko kuma ya yi fushi in ta ƙi yin hakan. Kuma ya wajaba akan miji ya ji tsoron Allah a cikin al’amuransa”.

A ƙarshe, abin da za a iya cewa shine, aikin gidan miji da mata s**a saba yi wani abu ne sananne a cikin al’adar Musulmi tun zamanin Manzon Allah (SAW) har zuwa yanzun da muke rayuwa. Matan aure sun kasance suna hidima wa mazajensu, suna dafa abinci suna wankin tufafin maigida da na yara, suna wanke-wanke da shara da kai ruwan wanka banɗaki da kula da yara da sauransu. Kuma wannan al’adar ba a taɓa samun wani zamani da al’ummar Musulmi ta yi inkarin ta ko ta yi tawaye gare ta ba.

Sannan kuma aikin gida da mata ke yi hanya ce ta samun lada da neman aljannar Allah (SWT). Amma kuma, bai k**ata miji ya ƙuntata wa matarsa ba ko ya sanya ta ayyuka masu wahala waɗanda ba za ta iya ba. Sannan kuma yana daga cikin hanyoyin kyautatawa, maigida ya dinga taya uwargida yana k**a mata aikin k**ar yadda Manzon Allah (SAW) yake yi. In kuma yana da hali da buƙata to ba laifi a ɗaukar mata mai aiki.

Allah shine mafi sani.

Kabir Asgar
26/03/2020

Address

Lagos

Telephone

+2348027820969

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kungiyar Raya Auren Sunnah Ta Kasa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share