11/09/2025
DAGA SHAFUN DDL HAUSA,,,,,KADDARA: Wani lamari mai tada hankali ya fito fili daga bakin wata mata bazawara, wacce ta bayyana irin mawuyacin hali da ta tsinci kanta a cikinsa tun bayan rasuwar mijinta.
Matar, wacce take da yara shida, biyu maza da kuma mata hudu, ta ce duk da arzikin da mijinta ya bari, hakan bai hana ta shiga cikin wani irin matsi na sha’awa da rudanin rayuwa ba.
A cewarta, duk lokacin da take shirin sake aure ko kuma ta kawo wani bazawari gida, yaranta sukan yi fito-na-fito da ita suna hana ta, suna cewa hakan zai tunasar da su da mahaifinsu. Wannan tsayayya ta yaranta ta jefa ta cikin ruɗani har ta fara neman mafita ta hanyoyi marasa dacewa.
“Na shiga harkar madigo, saboda kawai neman sassauta sha’awar da take damuna. Sau da dama nakan yi amfani da wasu ’yan uwana mata ko kuma abokiyar aiki. Har ma in k**a ɗaki a hotel domin kada yarana ko ’yan uwan mijina su gano sirrina,” in ji matar cikin kuka.
Ta kara da cewa kasancewarta malamar makarantar mata ya sa wani lokaci take amfani da bayanan da take yi wa daliban manya kan rayuwar aure wajen lura da wadanda sha’awarsu ke motsawa, sannan daga baya ta iya jawo su domin biyan bukatunta.
Sai dai matar ta bayyana cewa duk lokacin da ta aikata hakan, sai ta kamu da nadama mai tsanani, ta yi tuba, amma daga baya ta sake komawa. “Kullum nakan yi alwashin daina, amma na kasa. Na gaji da wannan rayuwa,” ta ce cikin hawaye.
A ƙarshe, ta roki malamai da al’umma da su taimaka mata da shawarwari kan yadda za ta guji wannan dabi’a da ta kira mugun aiki, domin samun kariya daga fushin Allah da kuma samun rayuwa mai tsarki.